12/01/2026
JAGORA (H) YA RUFE MU’UTAMAR DIN SHAHIDAI MASU RAI
Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)
Da yammacin ranar Lahadi, 22 ga watan Rajab 1447 (11/1/2026) ne Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya rufe Mu’utamar din Shahidai Masu Rai na Harka Islamiyyah a gidansa da ke Abuja.
A yayin jawabinsa, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya jawo hankalinsu akan fahimtar sadaukarwa a matsayin muhimmin abu a kokarin raya tafarkin Allah Ta’ala. Yace: “Wannan tafarki na sadaukarwa a tafarkin Allah, wani abu ne zaunanne, wanda yake da shi ne ake samun manya-manyan darajoji.”
Ya bayyana yadda Allah Ta’ala ke gwada sashen bayinSa Muminai da sashen fajirai ma’abota duniya. Yace: “Ana gwada mu da juna ne, aga cewa ko za mu daure.”
Harwayau, Jagora ya yi sharhin aya ta 155 a cikin suratul Baqara, da ke bayanin albishir din Allah Ta’ala akan jarabta Muminai. Yace: “Za mu gwada ku da wani abu na tsoro, da yunwa, da tawayan dukiya, da na rai da jiki ‘anfusi’, da ‘thamarat’”
Yace: “Kamar Shahidai masu rai kenan, wani ya rasa hannu, a rasa ido, a rasa kafa, a rasa kunne, a yi fama da rashin lafiya. Shi ma tawaya ne na ‘Nafs’. Da kuma ‘thamarat’, natijoji, kasuwanci ne mutum yake yi, ko kiwo ne, duk dai ya zama ya samu tawaya a rayuwarsa. To amma wannan ita ce hanyar, don haka aka ce, ka yi ma masu dauriya albishir.”
Jagora yace: “Dama gwaji ne, lamuhalata. An gwada na farko, kuma za a gwada na karshe. Duk lokacin da kace za ka yi addini lamuhalata za a gwada ka. Dole gwaji zai zo.”
Shaikh Zakzaky ya bayyana takaicinsa akan yadda wasu s**a dauka zaman lafiya tare da azzalumai shi ne addini. Yace: “Mu mun gode ma Allah muna makarantar Imam Husaini (AS). Makarantar Imam Husaini (AS) ta nuna mana cewa sadaukarwa ake yi a tafarkin Allah Ta’ala.”
Ya ba mahalartan kissoshin Shahidai masu rai daban-daban, da darussan dauka daga sadaukarwarsu. Inda yace: “A daure, kuma a dake. Maganin kenan.”
Da yake tsokaci dangane da halin da ake ciki a Jamhuriyar Musulunci a wannan tsakanin, Jagora (H) ya bayyana abin a matsayin shirin makiyan waje. Wanda kuma yace, Alhamdulillah tun yanzu sun fara gane sun yi asara.
Ya kuma yi tsokaci akan halin da muke ciki a wannan kasar na kai hare-hare da sunan ta’addanci, da kuma yadda Trump ya fara kawo hari a Sakkwato da sunan ceton Kiristoci. Yace: “Shin akwai ‘record; din ana kashe Kiristoci ne a Sakkwato? Akwai ma ‘record’ din ana kashe kiristoci a Nijeriya ne ma? Su wadanda ake ce ma ‘yan ta’addan nan, Amerika s**a yi su. Kayansu ne, su s**a assasa su suke ka* she mutane. Kayansu ne, amma kuma wai za su zo su cece ku daga gare su.”
Ya bayyana cewa, abu mafi muni shi ne cewa wai Kiristoci ake kashewa. “Da zai zo yace, zai ceci kasar nan daga ta’addanci. Za mu ce shiri ne, su s**a yi ‘yan ta’addan. Amma wai a’a, wai zai ceci kirista ne daga Musulmi.”
Shaikh Zakzaky ya nuna takaici akan yadda mutane s**a yi tsit da bakinsu akan wannan, amma kuma suna tsoma baki akan Iran.
Yace: “Shi Shaidan ba bari yake ba, za a cigaba ne. Yadda kuka ga ba su kyale Jamhuriyar Musulunci ba duk da cika shekara 47 da samunta a bana … Su ma fa kenan. Ballantana kuma kullum tunanin da suke yi akanmu shi ne, haka fa s**a yi wasa da abinda ya d**o a Iran, don haka (s**an ce) kar ku yi wasa da wadannan. Shi yasa kullum suke nufinmu, suna cewa, (in aka bar mu wai) sai mun kwace kasar.
“Har suna cewa, za mu kwace Abuja. To ai dama kayanmu ne! Shirmensu kawai, wai ba za a yi ‘program’ a nan ba. To sun taba hana wani ‘program’? Sai dai su hana a wani wuri a je a yi a wani wuri ko? To sun ci riban mene? Akwai lokacin kuma da ba zai yiwu ba. Yana nan zuwa kuma. Hanya guda ne, za su bude wuta, illa iyaka.”
Ya bayyana yadda bara wancan aka yi Nisfu Sha’aban a sansanin sojojin sama da ke Abuja, aka gama lafiya lau, amma bara da aka zo yi a wurin, sai ga mota 41 na soja da ‘yan sanda s**a zo s**a yi barazanar bude wuta akan sai an tashi. Yace: “Kullum kishin ruwan za su bude wuta ne, aikin kenan kullum.”
Yace: “Muna fadin wannan ne don a san cewa, ba wai al’amura sun kawo karshe ba ne, za a cigaba ne. Kuma sadaukarwa za a cigaba da yi ne, insha Allahu har izuwa ga nasara.”
A karshe, Jagora ya rife da addu’ar Allah Ta’ala Ya karbi Shahadar Shahidanmu, Ya ba da lafiya ga Shahidai masu rai da marasa lafiya, Ya gaggauta kwato wadanda suke tsare. Ya bamu sabati har izuwa karshen al’amari, da nasara ko muna raye ko bamu raye.
22/Rajab/1447
11/01/2026