02/05/2026
ADDININ MUSULUNCI A GARƘI HAUSA.
DAGA KUNGIYAR GARKI YOUTH HAUSA DEVELOPMENT AND CULTURAL ASSOCIATION.
Musulunci hanya ce cikakkiya ta rayuwa wadda ke tafiyar da dukkan fannoni na rayuwar ɗan Adam—ibada, tsarin rayuwa, al’adu, ilimi, siyasa, neman arziki, da hulɗa da sauran mutane. Haka kuma yana nufin cikakken miƙa wuya da biyayya ga nufin Allah. An shigar da wannan addini a Arewacin Nijeriya ta hanyar kasuwancin sahara (trans-Sahara) daga Arewacin Afirka kusan ƙarni na 9, sannan ya bazu a cikin masarautun Hausa ta hannun ‘yan kasuwa.
A Garƙi Hausa, ilimin Musulunci ya daɗe yana wanzuwa. A farkon lokaci, ana samun wannan ilimi ne ta hanyar makarantu allo (makarantun Larabci), galibi a gida, a ƙarƙashin inuwa itatuwa, ko a masallaci. Karatun Alƙur’ani da haddace shi su ne manyan hanyoyin koyarwa a wancan lokaci. Daga baya kuma, an kafa makarantu irin na marigayi Mallam Liman, Mallam Sulaiman Danjaki, Mallam Usman (Malam Mai Bulala), Mallam Shua’ibu—Madrasatul Hidaayatu Ilaa Deenil Islamiya, Mallam Chindo Islamiya, Mallam Audu da sauransu. A halin yanzu, akwai makarantar Islamiya ta al’umma mai suna Madrasatul Ummul Qura Islamiya, wadda ke taka muhimmiyar rawa wajen ilmantar da matasan Garƙi game da addinin Musulunci.
A wasu lokuta, ɗalibai suna ƙara zurfafa iliminsu na Musulunci musamman a manyan masarautu da kuma a garin Keffi na jihar Nasarawa, inda da dama daga cikinsu s**a zama limamai da malamai, suna taimakawa wajen yaɗa addinin Musulunci. Misali, babban limamin ƙauyen Garƙi a halin yanzu, Abubakar Abdullahi, ya taɓa zama ɗalibi sannan kuma malami a makarantar Madrasatul Hidaayatu Ilaa Deenil Islamiya da ke Garƙi Hausa. Mutane suna samun jin daɗi daga tarukan zamantakewa da na tarbiyya, wanda hakan ya taimaka wajen karɓuwar Musulunci har ma da musuluntar wasu daga cikin ‘yan uwansu na Gbagyi a ƙauyen Garƙi.
YOUTH HAUSA DEVELOPMENT AND CULTURAL ASSOCIATION.