14/05/2026
Ko da an dora min bindiga a kaina ba zan wuce shekara hudu a kan mulki ba — Peter Obi
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana cewa idan aka zabe shi shugaban kasa zai yi wa’adin mulki guda daya kacal na shekaru hudu.
Obi ya bayyana hakan ne a wata hira da aka shirya watsawa a gidan talabijin na News Central TV, inda ya ce ko da an dora masa bindiga ba zai zauna fiye da shekaru hudu a mulki ba.
Ya ce yana son yin wa’adi daya ne domin tabbatar da daidaito da kwanciyar hankali a kasar.
Tsohon gwamnan jihar Anambra ya kuma soki manufofin tattalin arzikin gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman batun karbar bashi da tashin farashin rayuwa, yana mai cewa Najeriya na cikin mawuyacin hali na tattalin arziki.
A zaben shugaban kasa na 2023, Obi ya zo na uku bayan Tinubu na jam’iyyar APC da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP.