25/12/2023
Jami'an Tsaro Sun Koma Tamkar Almajirai A Kasar Nan
Daga : Abdul Rahaman Abdul Rahaman
Tun daga Abuja har Kebbi duk jami'in da ya tsayar da ni babu abin da yake tambayata na daga dangin ababen da s**a saba tambaya fa ce maula!
Haka a nan cikin kebbi ban taɓa cin karo da ma'aikatan MTD da ba su min maula ba. Ma'aikatan hukumar kiyaye haddura kuwa wannan kullum ne idan har na tsaya a danja.
Mafi yawan su sun jingine jigon aikin su sun duƙufa neman kuɗi domin nemawa iyalansu abinci. Ba ruwan su da hanyar da suke bi domin ciyar da su. Su dai ko ta yaya su samu su kai musu.
Albashin su tamkar babu yake idan har aka kwatanta da halin da aka tsinci kai. Gwabnati kuma ta sani ba wai bata sani ba, amma an kawar da kai.
Waƴannan fa ma'aikatan tabbatar da tsaro kenan. Ina ga sauran ma'aikata da suke zaune a ofis domin zartar da tsari da ƙudirin Gwabnati?
A yanzu muddin kana son biyan buƙata a Gwabnatance sai ka ware kuɗin cin hanci da rashawa. Saɓanin haka sai dai ka yi ta gararamba tsakanin ofisoshi babu mai kula ka.
Hatta asibitoci yanzu sai kana bayar da cin hanci kafin ka samu ganin ƙwararren likita, sai dai idan asibitinsa za ka je.
Da sannu saboda sakacin Gwabnati, tana neman sunnanta cin hanci da rashawa tsakanin ma'aikata.