14/05/2026
🔥 ZOBEN DA YA MALLAKI RAI — Part 12 🔥
🩸 “Akwai wata hanya ta uku…” 🩸
Duk s**a tsaya cak. 😨
⚡ Sarauniyar farko ta juya cikin fushi. “TSAYA SHI!” 😡
Amma muryar jaririn ta ci gaba.
👶 “Idan aka karya zoben da jinin wanda ya ƙirƙire shi… ƙofar za ta rufe har abada.”
Zainab ta girgiza kai cikin ruɗani. “Wanda ya ƙirƙire shi? Wa ya ƙirƙire zoben?” 😳
Sai AZHAR ya rufe idanunsa a hankali.
💀 “NI.” 💀
😨😨😨
“AZHAR?!” 😭
Maryam ta ja baya cikin tsoro. “Ina nufin… kai ne ka fara komai?”
Sai AZHAR ya yi murmushin baƙin ciki.
😈 “Tun kafin duniya ta manta da sunana… na kasance mutum ne.” 🩸
⚡ Nan take hotuna s**a bayyana a sararin sama.
🕯️ Wani tsohon masanin sihiri tsaye cikin daji. A gabansa akwai matar da yake so tana mutuwa saboda wata cuta. 😭
Sai ya yi ihu:
💔 “Ko da raina ne… zan ceci ki!”
Ya zuba jininsa cikin wani ƙaramin ƙarfe. 💍 Zoben ya fara haske.
💀 Amma wani abu daga duhu ya amsa.
“Za ka ceci mutum ɗaya… amma za ka buɗe ƙofar duhu har abada.” 🌑
😨 Zainab ta kalli AZHAR da hawaye.
“Saboda soyayya…?” 😭
Sai ya ɗaga kai a hankali.
😈 “Soyayya ce ta mayar da ni abin da nake yanzu.”
⚡ Sarauniyar farko ta yi ihu cikin fushi.
👑 “KADA KA BA SU BEGE!”
Nan take rundunar aljanunta s**a fara matsowa.
🖤 Idanu ja. Dogayen hannaye. Muryoyi k**ar iska daga kabari. 😨
Sai AZHAR ya miƙa hannu ga Zainab.
💀 “Ki yi sauri… kafin ƙofar ta buɗe gaba ɗaya.”
😰 “Me zan yi?!”
“Ki caka zoben cikin zuciyata.” 💍🩸
“A’A!” 😭
“In ba ki yi ba… duk duniya za ta shiga duhu.”
💥 Ƙasa ta sake fashewa. Gidaje suna nutsewa cikin baki. 🌍⚫
Mirror ɗin Inna da Baba ya fara ɓacewa.
“Inna!!” 😭
Sai mahaifiyarta ta yi murmushi cikin hawaye.
🥺 “Ki ceci duniya, ‘yata…”
⚡ Hannun Zainab na rawa sosai.
Ta kalli AZHAR. Karon farko— idanunsa ba su da tsoro ko mugunta.
Sai dai baƙin ciki. 💔
😈 “Da ace na taɓa samun dama ta biyu…”
Sai Sarauniyar farko ta yi ihu:
👑 “TA KASHE SU DUK!” 💀
🖤 Rundunar aljanu s**a fara gudu zuwa gare su.
⚡ Zainab ta rufe idanunta da ƙarfi.
“Ka yafe min…” 😭
Sai ta ɗaga zoben—
💍✨
…ta caka shi cikin zuciyar AZHAR.
😨 SHIRU.
Sai idon AZHAR ya buɗe sosai.
🩸 Jini baki ya fito daga bakinsa.
Amma…
😳 ya yi murmushi.
💀 “Na gode… Zainab.” 💀
💥 Nan take— zoben ya fashe da wani haske mai ƙarfi k**ar rana! ☀️⚡
Sarauniyar farko ta yi ihu mai razana.
👑 “A’A!! BA ZAI YUWU BA!!”
🖤 Dukkan aljanun s**a fara ɓacewa cikin toka.
⚡ Ƙofar duhun sama ta fara rufewa a hankali.
Sai Maryam ta kalli Zainab cikin hawaye.
👧 “An ƙare…”
Amma kafin hasken ya mutu gaba ɗaya…
😨 Zainab ta ji wata murya a kunnenta.
Muryar AZHAR.
💀 “Ki duba hannunki…” 💀
Ta sauko da idanunta a hankali.
😳 Sai ta ga—
💍 WANI SABON ZOBE ya bayyana a yatsarta. 🩸
Zanci gaba… ✍️🔥