31/01/2026
An K**a Wasu Ma’aurata Bisa Zargin Yi Garkuwa Da Kansu, Tare Da Karɓar Naira Miliyan 10 Matsayin Kudin Fansa.
Binciken Manema Labarai ya gano cewa ma’auratan, masu suna Fred da Goodness, sun ƙirƙiri labarin sacewar a ranar 7 ga watan Janairu domin neman kuɗi ga mijin, wanda ya yi niyyar komawa Amurka saboda rashin tallafin kuɗi.
Wani jami’in ’yan sanda da ya yi magana da Jaridar a ranar Alhamis ya ce ma’auratan sun tuntubi ’yan uwa daga danginsu, suna ikirarin cewa an sace su tare da neman kudin fansa.
Dangin sun tattara Naira miliyan 10 cikin kwana uku, suna zaton kuɗin zai taimaka wajen kubutar da su.
Jami’in ya ce ma’auratan sun tsara wurin karɓar kuɗin a wata makaranta da ke Cappa, Mushin.
“Jami’an da ke sa ido sun lura da matar ta shiga wurin ita kaɗai, daga baya mijin ya iso. Amma an fara zargin su bayan sun fito tare da jakar kuɗi. An bincika jakar, aka gano kudin fansa, nan take aka k**a su,” in ji shi.
Matar ta bayyana cewa ita ce ta shawarci mijinta su kitsa wannan shiri.
Tuni dai aka mika su ga ’yan sanda, inda bincike ya tabbatar da cewa su s**a kitsa garkuwar da kansu.
Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, Abimbola Addebisi, ta tabbatar da lamarin, tana mai cewa za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.
----Majiya Inda Ranka Freedom Fm Kano----
Kuyi Following Domin Kasancewa Tare Damu Arewa Post tv Tsintsiya Daya. 07065517311