10/04/2025
Fadar Shugaban kasa ta nemi afuwa bisa tabka kuskure wajen fitar da jadawalin sunayen nade-nade na gwamnati
Fadar Shugaban kasa ta nemi gafara bisa kuskuren da aka samu a cikin jerin sunayen nade-naden da ta fitar domin yin raddi ga zargin nuna bangaranci da ake yi wa Shugaba Bola Tinubu dangane da nade-naden da yake yi.
Nade-naden Shugaban kasar na baya-bayan nan sun zama abin muhawara, inda ‘yan adawa ke zarginsa da fifita mutanen yankinsa fiye da sauran yankunan Najeriya.
A wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise, Sanata Ali Ndume, dan majalisar dattijai daga APC mai wakiltar Borno ta Kudu, ya zargi Shugaban kasa da karya tsarin wakilcin kowa da kowa a nade-naden sa.
Ndume ya bayyana cewa ya yanke shawarar jawo hankalin Shugaban kasa kan wannan al’amari ne saboda yana da damar yin s**a, duk da cewa suna jam’iyya daya.
A kokarin karyata zargin, Fadar Shugaban kasa ta saki jerin sunayen mutanen da Shugaba Tinubu ya nada da kuma yankunan da s**a fito.
A cewar jerin, an bayyana cewa Shugaban kasa ya nada mutane 29 daga Kudu maso Yamma — yankinsa na asali, 35 daga Arewa maso Yamma, 22 daga Kudu maso Kudu, 16 daga Kudu maso Gabas, 25 daga Arewa ta Tsakiya, da kuma 24 daga Arewa maso Gabas.
Sai dai masu s**a sun ce jerin bai cika ba, domin wani babban hadimi daga yankin Shugaban kasa bai shiga cikin jerin ba.
Rashin saka sunan Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, a cikin jerin, ya kara karfafa hujjar da ake yadawa cewa gwamnatin Shugaba Tinubu na nuna bangaranci, musamman ganin yadda yankin Kudu maso Gabas ke da karancin wakilci a cikin gwamnati.
“Mun lura da wasu kurakurai a jerin sunayen nade-naden da muka wallafa. Muna bada hakuri. Za mu wallafa sabon jerin da aka gyara nan gaba. Mun gode,” in ji Dare a shafinsa na X.
Sai dai Dare bai bayyana dalilin da ya sa aka bar sunan Gbajabiamila a waje ba.
🖊ATP News
📸Flash News