11/06/2026
Shugabannin Gamayyar Ƙungiyar ’Yan Kasuwa ta Jihar Bauchi, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abdallah Caps, sun kai ziyarar girmamawa ga Hon. Dr. Yakubu Adamu, ɗan takarar gwamnan Jihar Bauchi na Jam’iyyar APM, domin taya shi murnar samun tikitin takara tare da bayyana cikakken goyon bayansu ga tafiyarsa ta siyasa.
A yayin ziyarar, shugaban ƙungiyar ya bayyana cewa sun yanke shawarar mara wa Hon. Dr. Yakubu Adamu baya ne sakamakon nagartarsa, jajircewarsa da kuma irin hangen nesan da yake da shi wajen kawo ci gaba ga jihar.
Shi ma da yake jawabi, Hon. Sulaiman Mohammed Bello ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Bauchi da ta cika alkawarin tallafin da ta yi wa ƙungiyar, yana mai bayyana cewa sun fara ganin alamun aiwatar da wannan alkawari, tare da fatan za a kammala shi cikin gaggawa.
A nasa martanin, Hon. Dr. Yakubu Adamu ya nuna matuƙar godiya ga shugabannin ƙungiyar bisa wannan ziyara da kuma irin goyon bayan da s**a nuna masa. Ya tabbatar da aniyarsa ta ci gaba da aiki tukuru domin samar da ci gaba mai ɗorewa da bunƙasa tattalin arzikin Jihar Bauchi idan aka ba shi dama.
An kammala taron da addu'o'in neman zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba ga Jihar Bauchi da al'ummar Najeriya baki ɗaya.